Tsananin zafi ya kwantar da mahajjata 6,700 a Saudiyya

Date:

Cibiyoyin dake kula da waɗanda zafin rana ya illata a wuraren ibada masu tsarki na ƙasar Saudiyya na ci gaba da samun hauhawar mutanen da ake kwantarwa saboda jigata.

Ana alaƙanta lamarin da gazawar mahajjata wajen bin ƙa’idojin kare kai daga tsananin zafin rana da ake a kasar Saudiyya.

Tallah

Ma’aikatar Lafiya ta Saudiyya ta faɗakar da mahajjata game da hatsarin tsananin zafin rana, inda ta buƙace su da su riƙa sanya ɓaƙin tabarau da kuma shan ruwa sosai, sannan su guje wa zirga-zirgar da ba ta wajaba ba.

Ganduje ya Magantu kan dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 da gwamnatin Kano ta yi

Haka nan ma’aikatar ta buƙaci maniyyatan da su guje wa tsayuwa na tsawon lokaci.

BBC Hausa ta rawaito Ma’aikatar ta ce a halin yanzu waɗanda tsananin zafin ranar ya kwantar sun kai 6,700 tun bayan fara aikin hajjin bana.

A jiya an samu irin wannan matsala mafi yawa, inda zafin ya illata mutum 2,200, cikinsu har da mutum 261 waɗanda suka shiga mummunan yanayi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...