Abba Gida-gida ya dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 gwamnatin Ganduje ta dauka aiki

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin dakatar da biyan albashin ma’aikata 10,000 wadanda gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ta dauka aiki, har sai an gudanar da bincike.

 

Akanta Janar na jihar Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana haka ga manema labarai a Kano .

Tallah

Abdulsalam ya ce ma’aikatan da abin ya shafa sun yi aiki ne a ƙarshen gwamnatin da ta gabata.

Cutar Zazzabin Maleria ta bulla a kasar Amuruka

Ya ce an kafa wani kwamiti da zai binciki yadda aka dauke su aiki a ma’aikatun gwamnati, inda ya tabbatar da cewa sakamakon bincike ne zai sa asan makomarsu wadanda abun ya shafa.

Tallah

Akanta Janar din ya kuma sanar da dakatar da sauya wuraren aikin da gwamnatin da ta gabata ta yi wa wasu ma’aikatan, Inda ta bukaci kowa ya koma Inda yake tun da farko.

Abdulsalam ya bayyana shirin sabuwar gwamnati na biyan albashin ma’aikata a ranar 25 a kowane wata, domin ya bayyana cewa za a biya ma’aikatan da suka yi ritaya hakkokin yadda ya kamata.

Ya kuma bayyana cewa sabuwar gwamnatin za ta yi aiki da asusu guda domin magance zurarewar kudaden gwamnati .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...