Daga Rahama Umar Kwaru
Kwamishinan ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Hon. Umar Haruna Doguwa ya jaddada Shirin sa na tabbatar da kudurin Gwamnatin Jihar domin farfado da darajar Ilimi.
Yayi wannan kalami ne a yayin ganawar sa ta farko da manyan ma’aikatan ma’aikatar tare da mukaddasan shugabannin Sassa dake karkashin ma’aikatar a ofishin sa.
Abba Gida-gida ya dakatar da albashin maβaikata dubu 10 gwamnatin Ganduje ta dauka aiki
Kwamishinan ya ce Babban burin sa shine yaga cewa ya taimaka wajen dawo da daraja da martabar Ilimi a jihar Kano wanda ya sami tasgaro mai yawa a shekarun da suka gabata.

Ya Kara da cewa makasudin ganawar sa da Ma’aikatan shine domin su san juna, sannan Kuma su yi masa bayani akan yadda ayyukan su suke domin samun makamar tafiyar da nasa aikin.
Kwamishinan ya tabbatar wa da Ma’aikatan cewa shi mutum ne wanda yake son aiki da mutane masu kwazo da rikon amana wajen gudanar da ayyukan su.

Hon.Doguwa yace a zaman da zai yi na aiki a wannan ma’aikatar bashi da burin ya musgunawa kowa, burin sa kawai yaga kowa Yana aikin sa yadda yakamata.
” Amma Ina mai tabbatar muku da cewa duk wanda bazai bani hadin Kai muyi aiki ba to tabbas zan sa ayi waje dashi na sami chanjin sa domin aikin mu yayi kyau mu samu mu kyautata harkar Ilimi a Jihar Kano” in ji kwamishina Haruna Doguwa.
Kwamishinan wanda ya yaba da yadda yagan fasalin Ma’aikatan, yace idan suka zama masu Kara jajircewa to babu shakka bukatar sa zata biya wajen gudanar da aikin da’aka dora Masa alhakin aiwatar wa.
Daga karshe ya bayyana cewa zai yi aiki da kofofin ofishin sa a bude domin basu dama su bijiro da dabarun aiki iriiri don bunkasa ilimi a jahar Kano.