Abba Gida-gida ya dakatar da albashin ma’aikata dubu 10 gwamnatin Ganduje ta dauka aiki

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin dakatar da biyan albashin ma’aikata 10,000 wadanda gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ta dauka aiki, har sai an gudanar da bincike.

 

Akanta Janar na jihar Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana haka ga manema labarai a Kano .

Tallah

Abdulsalam ya ce ma’aikatan da abin ya shafa sun yi aiki ne a ƙarshen gwamnatin da ta gabata.

Cutar Zazzabin Maleria ta bulla a kasar Amuruka

Ya ce an kafa wani kwamiti da zai binciki yadda aka dauke su aiki a ma’aikatun gwamnati, inda ya tabbatar da cewa sakamakon bincike ne zai sa asan makomarsu wadanda abun ya shafa.

Tallah

Akanta Janar din ya kuma sanar da dakatar da sauya wuraren aikin da gwamnatin da ta gabata ta yi wa wasu ma’aikatan, Inda ta bukaci kowa ya koma Inda yake tun da farko.

Abdulsalam ya bayyana shirin sabuwar gwamnati na biyan albashin ma’aikata a ranar 25 a kowane wata, domin ya bayyana cewa za a biya ma’aikatan da suka yi ritaya hakkokin yadda ya kamata.

Ya kuma bayyana cewa sabuwar gwamnatin za ta yi aiki da asusu guda domin magance zurarewar kudaden gwamnati .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...