Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya bayyana ranar da zai rantsar da sabbin kwamishinoni

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa zai jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni a ranar litinin 26 ga watan Yuni na shekara ta 2023.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ofishin Sakataren gwamnatin jihar kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi a yammacin wannan rana.

Hajjin bana: An Sami masu tabin hankali a Mahajjatan Najeriya, yayin da mutane 6 suka rasu a Saudiyya

Sanarwar tace za’a rantsar da sabbin kwamishinonin ne a dakin taro na Africa House dake gidan gwamnati da misalin karfe 11 na safe.

Wata Kotu a Kano ta hana Abba Gida-gida rushe wasu gine-gine a jihar

Idan za’a iya tunawa a makon da ya gabata ne majalisar dokokin jihar kano ta tantance tare da Amincewa da mutane 17 cikin 19 da gwamnan ya aike mata da sunayen su domin tantancewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...