NDLEA ta rufe wani gidan mai da aka boye tabar wiwi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nigeria NDLEA reshen jihar Neja ta rufe gidan man da ake zargin ana amfani da shi a matsayin wajen boyewa da sayar da tabar wiwi .

 

Kwamandan hukumar na jihar, Musa Bwalin, ne ya shaidawa manema labarai a Minna cewa an tsare jami’in tsaro da wasu ma’aikatan gidan man domin gudanar da bincike.

Hajjin bana: An Sami masu tabin hankali a Mahajjatan Najeriya, yayin da mutane 6 suka rasu a Saudiyya

Bwalin ya ce sama da shekara guda rundunar ta kama mutane 250 da ake zargi da sayar da miyagun kwayoyi daga cikin 64 da aka samu da laifi.

Wata Kotu a Kano ta hana Abba Gida-gida rushe wasu gine-gine a jihar

Ya kuma bukaci mazauna yankin da su daina kyamar masu shaye-shayen miyagun kwayoyi, maimakon haka jama’a su kusance tare da jan su a jiki ko zasu fahimci matsalolin don gyarawa.

Tallah

Ya bukaci gwamnan jihar Neja da ya taimaka wa rundunar da motocin aiki domin su samu damar shawo kan matsalar sayar da miyagun kwayoyi a fadin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...