Ƙungiyar ƙwadago za ta sake ganawa da gwamnatin Najeriya kan cire tallafi

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago guda biyu a Najeriya za su sake ganawa da jami’an gwamnati don kokarin ganin sun amince da sabon mafi karancin albashi da kuma wasu bukatu na ma’aikata bayan da Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur.

 

Janye tallafin ya jawo tashin farashin mai da tsadar sufuri.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya sake sabbin nade-naden mukamai

Ƙungiyar ƙwadago da TUC a Najeriya ta ce yau ne wa’adin da ta ba gwamnatin tarayya ke cika, kan bukatarta mayar da mafi karanci albashi naira dubu 200 sakamakon janye tallafin mai.

Ƙungiyar ta ce bukatar biyan mafi kakantar albashin naira dubu 200 na cikin bukatun da ta mika wa gwamnatin Tarayya, domin ragewa ma’aikata raɗaɗin wahalar janye tallafin mai da sabuwar gwamnatin ta yi.

Comrade Nuhu Toro, sakatare janarar da kungiyar ya faɗawa BBC cewa suna kan bakansu akan albashi mafi ƙanƙanta na naira dubu 200 wa ƙaramin ma’aikaci a Najeriya domin tsadar rayuwar da mutane suka shiga.

Ya ce “Farashin kayayyaki da rayuwa ma gaba daya tsada ya keyi, saboda haka gwamnati ba ta da hujja illa ta ƙara ma ma’aikata mafi ƙanƙantar albashi na naira dubu 200 domin su ma’aikata su suke ƙirƙirowa ta arzikin ƙasa”.

“Gwamnati za ta iya biyan wannan albashin idan ta rage almubazaranci, idan ta rage sama da faɗi da dukiyan talakawa, kuma idan ta rage kashe kuɗi a kan abubuwan da bai kamata ba.”

Toro ya dai ƙara da cewa dole ne gwamnati ta rage yawan kashe kudin da take yi, shi ne za ta sami yanda za tayi ta biya ma’aikata albashi mafi ƙanƙanta naira dubu 200.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...