Da dumi-dumi: Shugaba Tinubu ya karbi bakuncin Akpabio, Jonathan a fadar shugaban kasa

Date:

Daga Aisha Muhammad Adam

 

A halin yanzu dai shugaba Bola Ahmed Tinubu yana ganawa da sabon shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa, dake Abuja.

 

Haka kuma a ofishin shugaban kasar domin ganawa akwai gwamnan jihar Imo kuma shugaban kwamitin zaben majalisar dattawa na jam’iyyar APC, Hope Uzodinma wanda ke tare da tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje.

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

Shi ma gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu yana cikin fadar Villa.

A safiyar yau ne dai shugaba Tinubu ya karbi bakuncin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a ofishin sa.

Har yanzu babu cikakken bayani kan ganawar ta su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...