Da dumi-dumi: Shugaba Tinubu ya karbi bakuncin Akpabio, Jonathan a fadar shugaban kasa

Date:

Daga Aisha Muhammad Adam

 

A halin yanzu dai shugaba Bola Ahmed Tinubu yana ganawa da sabon shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa, dake Abuja.

 

Haka kuma a ofishin shugaban kasar domin ganawa akwai gwamnan jihar Imo kuma shugaban kwamitin zaben majalisar dattawa na jam’iyyar APC, Hope Uzodinma wanda ke tare da tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje.

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

Shi ma gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu yana cikin fadar Villa.

A safiyar yau ne dai shugaba Tinubu ya karbi bakuncin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a ofishin sa.

Har yanzu babu cikakken bayani kan ganawar ta su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...