Tajudeen Abbas ya zama Shugaban majalisar wakilai ta 10

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

An zabi Tajudeen Abbas, dan majalisa mai wakiltar mazabar Zaria a matsayin shugaban majalisar wakilai ta 10.

 

Tajudeen Abbas ya samu kuri’u 353 inda ya doke abokan takararsa biyu Idris Ahmed Wase da Aminu Sani wanda ya samu kuri’u 3 kowanne.

 

Benjamin Kalu wanda ba shi da abokin hamayya , an bayyana shi a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

 

Zababbun Mambobi dari uku da hamsin da tara ne suka kada kuri’a a yayin zaben shugabannin majalisr su biyu .

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

An dai gudanar da zaɓen ne ta hanyar kada hanyar kada kuri’a kamar yadda doka ta 10 ta Majalisar ta tsara.

Tsohon Shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhassan Ado-Doguwa ne ya gabatar da kuɗirin zabar sabon kakakin wanda Nnolim Nnaji mai wakiltar mazabar tarayya ta Nkanu ta Gabas/Nkanu ta Yamma kuma ya amince da shi.

 

Bayan kammala kada kuri’a wanda ya dauki sama da awa daya, magatakarda na majalisar wakilai Yahaya Danzaria ya sanar da Tajudeen Abbas a matsayin Shugaban Majalisar ta 10

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...