Sarakunan Kano da Bichi sun jagoranci Jana’izar limamin waje

Date:

Khadija Abdullahi Aliyu

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya jagoranci Sallar Jana’zar Marigayi Limamin Waje Wazirin Kano Murabus Sheikh Nisir Muhammad Nasir.

 

An dai gudanar da Sallar Jana’zar ne da Karfe 9:00am na safiyar ranar Alhamis dinnan ne a Kofar Kudu fadar Mai Martaba Sarkin Kano.

Kwankwaso ya nemi kotu ta kawace Nasarar wani dan majalisar tarayyar NNPP a Kano

Mai Martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero yana daga cikin manyan mutane da suka halarci Jana’zar, da sauran manyan Mutane da Shehunnai da limamai da Yan Kasuwa da sauran al’uma.

 

Bayan idar da Sallar Jana’zar ne Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Dan uwansa Mai Martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero da sauran daruruwan al’umma suka raka gawar Marigayin.

An dai binne marigayi Sheikh Nisir Muhammad Nasir ne a Makabartar Dan Dolo dake Gordon Dutse cikin yankin Karamar Hukumar Gwale dake Birnin Kano.

Mai Martaba Sarkin yayi addu’ar Allah ya gafarta masa yasa aljanna makoma a gareshi tareda baiwa iyalai da “Yan uwa da sauran al’uma hakurin jure rashin Wazirin Kano Murabus kuma Limamin Waje Sheikh Nisir Muhammad Nasir.

Da dumi-dumi: Bola Tinubu ya Magantu kan rushe gine-gine da gwamnatin Abba Gida-gida ke yi a Kano

Kafin rasuwarsa Sheikh Nisir Muhammad Nasir babban Amini ne ga marigayi Sarkin Kano Alhaji Dr. Ado Bayero Wanda ya bayar da gudunmawa a bangaroei daban daban ta hanyar cusa kyawawan dabi’u ga matasa da cusa musu soyayyar Annabi Muhammadu SAW.

Sheikh Nisir Muhammad Nasir ya rasu yabar matansa na aure da Yaya da kuma jikoki masu yawa.

Abubakar Balarabe Kofar Naisa
Babban Sakataren yada labarai na Masarautar Kano.
8/6/2023

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...