Janye tallafin man fetur ya janyo dogayen layi a gidajen mai a Nigeria

Date:

Dogayen layukan mai sun dawo a gidajen sayar da mai a fadin biranen Najeriya tun bayan da sabon shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man.

 

A jiya Litinin ne Tinubun ya sanar da cire tallafin a jawabinsa na farko bayan rantsuwar kama iaki inda ya ce kasafin ba ya cikin kasafin kudin da ya gada daga gwamnatin Buhari.

Wasu rahotanni na cewa a birane irin su Lagos da Abuja ana sayar da man a wasu wuraren a kan kusan naira 600 a kan lita daya kari daga daga 185 a kan lita a yau Litinin.

Sai dai kuma kamfanin mai na kasar NNPC ya sanar cewa akwai wadataccen mai a kasar saboda haka babu dalilin da zai sa mutane su shiga fargabar sayen man.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya Koka da yadda Ganduje ya bar masa bashi Mai tarin yawa

Ƴan kasar da dama na kokawa kan yadda suke shafe tsawon lokaci a kan layi domin sayen man.

 

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Tinubu ya ce za a yi amfani da kudin tallafi wanda ya ce a yanzu wasu attajirai ne kawai suke cin moriyarsa, wajen bunkasa wasu fannonin da jama’a za su fi amfana.

Ba a san ko tun daga jawabin nasa gwamnati ta dakatar da tallafin ba kenan.

Masana harkokin tattalin arziki na nuna cewa tasirin cire tallafin zai haddasa tsadar sufuri da kayayyaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...