Wahalar Mai: Tinubu ya gana da Emefiele, Kyari a Villa

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Shugaban kasa Bola Tinubu zai fara aikinsa a matsayin shugaban Najeriya tare da ganawa da gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele, da shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari a fadar gwamnatin tarayya .

Duk da cewa ba a bayyana makasudin taron a hukumance ba, jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa taron ba zai rasa nasaba da rikicin da ake samu na cire tallafin man fetur wanda tun daga lokacin ya jefa ‘yan Najeriya cikin fargaba.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Tinubu ya shiga fadar shugaban kasa a ranar Talata, inda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da wasu manyan jami’an gwamnati suka tarbe shi a kofar ofishinsa.

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da kakakin majalisar Femi Gbajabiamila da babban sakataren fadar shugaban kasa Tijjani Umar, tsohon kwamishinan kudi na Legas, Wale Edun; Dele Alake; James Faleke.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...