Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Gida-gida ya yi Sabbin nada-naden mukamai

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Gwamnan Jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya gudanar da nada-naden mukamin na farko a gwamnatin sa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Wadanda aka nada mukaman sun haɗa da:

1. Hon. Shehu Wada Sagagi, Shugaban Ma’aikata

2. Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jihar Kano

3. Dr. Farouq Kurawa
Babban Sakataren gwamnan wato PPS

4. Hon. Abdullahi Ibrahim Rogo, Shugaban tsare-tsare na gwamna

5. Sanusi Bature Dawakin Tofa, Babban Sakataren Yada Labarai

Sanarwar ta ce an zabi Wadannan nade-naden sun fara aiki ne daga yau Litinin 29 ga Mayu, 2023. Kuma an zabi wadanda aka nada ne bisa la’akari da tarihinsu, sadaukarwa da amincin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...