Daga Kamal Yahaya Zakaria
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ya bukaci ‘yan siyasa da su rika gina jama’a maimakon sace dukiyar al’ummar.
“Kudi ba shi ne komai ba, abun da ya fi dacewa kawai ku mai da hankali wajen inganta rayuwar al’ummar da suka zabo ku”. Inji Kwankwaso
Gobara ta tashi a Gidan da Ganduje ya Koma makonni biyu da suka gabata
Ya ba da wannan shawarar ne a Minna a ranar Alhamis, a lokacin da yayin wata lacca da aka shirya a cigaba da bukukuwan da ake gudanarwa gabanin rantsar da zababben gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago.
Idan kana son sayar da gine-ginen gwamnati ga abokanka da iyalanka, to ka bari sai ka bar ofis, lokacin ne za ka yi nadama,” inji Kwankwaso.
Zargin Kisan Kai: Ba mu da hujjojin da zasu tabbatar da zargin da ake yiwa Doguwa – Gwamnatin Kano
Tsohon gwamnan ya bukaci zababben gwamnan da ya zuba jari mai tsoka a fannin ilimi da tsaro domin amfanin jihar Neja ko kuma ya yi danasani a nan gaba, ya kara da cewa jarin da ake zubawa a fannin ilimi ba’a iya ganin shi nan take, amma a karshe zai haifar da sakamako kai kyau ga Kai da Kuma al’ummar da zaka shugabanta.
Ya kara da cewa idan Bago yana so zama gwamnan da zai taka rawar gani, to dole sai zage damtse ya fara aiki da zarar an rantsar da shi domin ci gaban al’ummar Neja da inganta tattalin arzikin jihar.