Ba zan baiwa ‘yan Nigeria Kunya ba – Tinubu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sha alwashin ba zai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba.

 

Tinubu ya bayyana haka ne bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama shi da lambar girmamawa ta kasa (GCFR) a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Ya ce ya fahimci karramawar da Kuma aikin da ke gabansa, inda ya yi alkawarin ba zai baiwa shugaban kasa da ‘yan Nijeriya kunya ba.

 

“Ni mutum ne mai saukin kai wanda ya ci gajiyar goyon baya da fatan alkhairin al’ummar Najeriya. Jama’a sun dogara gare mu, Ka yi aikinka nima zan yi nawa don inganta rayuwar al’ummar Nigeria .

“Idan na shigo faggen dole ne na yi abun da ya dace wajen inganta fannin tsaro, tattalin arziki, noma, ayyuka, ilimi, lafiya da wutar lantarki da kuma sauran bangarori , ya mai girma Shugaban kasa da kai da yan Nigeria dole ne in yaba muku in kuma fidda ku kunya.”

Ya godewa Buhari bisa karramawar da ya yi masa da kuma mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya samu kambun babban kwamandan Niger (GCON).

Ya kara da cewa sadaukarwar da Shugaban kasa ya yi na samar da kyakkyawan shugabanci ga dimokuradiyya ba abu ne mai sauƙi ba.

Tinubu ya kuma yaba wa shugaba Buhari bisa karrama marigayi MKO Abiola, wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka soke ranar 12 ga watan Yunin 1993.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...