Daga Rahama Umar Kwaru
Shugaban kasa Muhammadu Buhari mai barin gado, ya baiwa shugaban kasa mai jiran gado Asiwaju Bola Tinubu lambar girma ta kasa (GCFR).
Buhari ya karrama Tinubu ne a wajen taron da aka gudana a Abuja ranar Alhamis.
Da dumi-dumi: Ganduje ya mika muhimman bayanan gwamnatin Kano ga Abba Gida-gida
Wannan karramawar ta GCFR ta zo ne a wani bangare na Bikin mika mulki ga zababben shugaban kasa da mataimakinsa, Kashim Shettima.
Akwai masu shirin tayar da hatsaniya a lokacin rantsar da sabbin gwamnatoci a Najeria – DSS
Idan za’a iya tunawa cewa Buhari ya bayyana aniyarsa ta mika mulki nan da ‘yan kwanaki masu zuwa.
Shugaba Buhari sai zai mika mulki a ranar Litinin mai zuwa, 29 ga Mayu, ga zababben shugaban kasa, Bola Tinubu.