Mutane huɗu sun rasu a fashewar tukunyar gas a Sokoto

Date:

Akalla kimanin mutane huɗu ne suka rasu sakamakon fashewar tukunyar iskar gas a wani shagon mai akin walda da ke karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar DSP Sanusi Abubakar ya tabbatar wa Gidan Talabijin na Channels cewa fashewar ta auku ne a ranar Lahadi.

Sai dai ya ce fashewar ba ta da nasaba da rashin tsaro da ake fama da shi a yankin, illa tukunyar gas ce kawai ta fashe.

DSP Sanusi ya ce ba ya ga mutum huɗu da suka rasu, akwai wasu mutum uku da suka jikkata kuma suna karɓar magani a asibiti.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...