Mutane huɗu sun rasu a fashewar tukunyar gas a Sokoto

Date:

Akalla kimanin mutane huɗu ne suka rasu sakamakon fashewar tukunyar iskar gas a wani shagon mai akin walda da ke karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar DSP Sanusi Abubakar ya tabbatar wa Gidan Talabijin na Channels cewa fashewar ta auku ne a ranar Lahadi.

Sai dai ya ce fashewar ba ta da nasaba da rashin tsaro da ake fama da shi a yankin, illa tukunyar gas ce kawai ta fashe.

DSP Sanusi ya ce ba ya ga mutum huɗu da suka rasu, akwai wasu mutum uku da suka jikkata kuma suna karɓar magani a asibiti.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...