Goodluck Jonathan ya bayyana abin da yake hana shi barci a fadar shugaban kasa

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Tsohon shugaban kasar Nigeria Goodluck Jonathan ya ce rashin tsaro ya sa shi “mummunan ciwon kai” a lokacin da yake rike da shugabancin Najeriya.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da aikin titin mai tsawon kilomita 22 a jihar Taraba.

A cewarsa, yana kwana bai yi barci ba sakamakon kokarinsa na magance matsalar tsaro a wancan lokaci.

Tsohon shugaban kasar ya bukaci al’ummar jihar da su zauna lafiya domin a samu ci gaba.

Jonathan, wanda ya bayyana cewa tsaro yana hannun jama’a, ya bayyana farin cikinsa yadda a hankali Taraba ke komawa cikin kyakkyawan yanayin zaman lafiya da juna.

“Lokacin da nake shugaban Najeriya, rashin tsaro ya sa na kasa barci. Wani lokaci ma yayin da nake coci, ADC na ya kan kawo waya ta ya nuna min yadda ake kashe mutane ko sace mutane, kuma hakan yana da na sami ciwon kai kuma na kasa barci.”

“Lokacin da na shigo filin jirgin sama na Jalingo, da na ga Daraktan DSS, sai na yi sauri na tambaye shi, ‘Yaya akai jami’an tsaron jihar Taraba suke da himma?’ sai ya ce min mutanen ‘Taraba na son zaman lafiya da kwanciyar hankali’,” a cewar Jonathan

Jonathan ya zama shugaban Najeriya daga 2010 zuwa 2015

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...