Da dumi-dumi: Sarkin Musulmi ya tabbatar da ganin watan Sallah a Nigeria

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad III ya sanar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya.

Yanzu-Yanzu: An ga watan karamar Sallah a Saudiyya

Sarkin Musulmin ya ce ganin jinjirin watan da aka yi a a kasar ya sanya ranar Juma’a 21 ga watan Afrilu, 2023 ta zamo 1 ga watan Shawwal, 1444.

Rarara ya Magantu kan korar yan sandan dake bashi kariya

Kwamitin tantance ganin wata karkashin jagorancin Maigirma Wazirin Sakkwato Farfesa. Sambo Wali Junaidu ne ya jagoranci aikin tabbatar da ganin watan a bana.

Akasarin Musulmai a fadin duniya dai sun tashi da Azumin watan Ramadan ranar 23 ga watan Maris 2023.

Saudiyya tuni ta sanar da ganin watan a garin garin Tumair wanda hakan ke nufin ranar Juma’a ne sallah. Ko da yake da farko sai da ta ba da sanarwar ba a ga watan ba a lardun gashin ƙasar.

A Iran kwamitin ganin watan ƙarƙashin jagorancin shugaban addini na ƙasar Ali Kamenei ya ce ba a ga watan ba, don haka sallah sai ranar Asabar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...