Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Kimanin ‘yan mata ‘yan makaranta 42,954 ne suka bar zuwa makaranta tsakanin Yuli 2021 da Yuni 2022 bayan sun sami juna biyu.
Wannan dai na zuwa ne a wani sabon rahoto da babban mai binciken kudi na kasar Tanzaniya (CAG) ya fitar ranar Litinin.
Likitoci a Najeriya sun soki sabon ƙudurin Majalisar wakila ta ƙasa
Rahoton CAG na shekarar 2021 zuwa 2022 da aka gabatar a majalisar dokokin kasar a Dodoma babban birnin kasar, ya ce daga cikin ‘yan mata 42,954 da ke da ciki, 23,009 sun fito daga makarantun sakandare, 19,945 kuma sun fito daga makarantun firamare.
An haramtawa limamai karanta Qur’ani daga wayar hannu a lokacin Tarawi da Tahajjud
Rahoton ya ce ‘yan matan sakandare da sukai yi ciki sun kai kashi 28 cikin 100 na ‘yan mata 82,236 da aka shirya zasu kammala karatunsu a shekarar 2021.
Rahoton ya ce, ga makarantun firamare, karamar hukumar Kwimba da ke yankin Mwanza ce ta fi kowacce yawan yara mata masu ciki a tsawon lokacin da akai bitar tare da ‘yan mata 9,045, sai kuma karamar hukumar Uvinza da ke yankin Kigoma da ke da ‘yan mata 2,172 suka yi ciki kamar yadda rahotan ya nuna. (NAN)