‘Yan mata sama da dubu 42 ne suka daina zuwa makaranta saboda sun yin ciki – Rahoto

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Kimanin ‘yan mata ‘yan makaranta 42,954 ne suka bar zuwa makaranta tsakanin Yuli 2021 da Yuni 2022 bayan sun sami juna biyu.

 

Wannan dai na zuwa ne a wani sabon rahoto da babban mai binciken kudi na kasar Tanzaniya (CAG) ya fitar ranar Litinin.

Likitoci a Najeriya sun soki sabon ƙudurin Majalisar wakila ta ƙasa

 

Rahoton CAG na shekarar 2021 zuwa 2022 da aka gabatar a majalisar dokokin kasar a Dodoma babban birnin kasar, ya ce daga cikin ‘yan mata 42,954 da ke da ciki, 23,009 sun fito daga makarantun sakandare, 19,945 kuma sun fito daga makarantun firamare.

An haramtawa limamai karanta Qur’ani daga wayar hannu a lokacin Tarawi da Tahajjud

 

Rahoton ya ce ‘yan matan sakandare da sukai yi ciki sun kai kashi 28 cikin 100 na ‘yan mata 82,236 da aka shirya zasu kammala karatunsu a shekarar 2021.

 

Rahoton ya ce, ga makarantun firamare, karamar hukumar Kwimba da ke yankin Mwanza ce ta fi kowacce yawan yara mata masu ciki a tsawon lokacin da akai bitar tare da ‘yan mata 9,045, sai kuma karamar hukumar Uvinza da ke yankin Kigoma da ke da ‘yan mata 2,172 suka yi ciki kamar yadda rahotan ya nuna. (NAN)

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...