Kammala zaben 2023: Abba Gida-gida ya baiwa shugabannin kananan hukumomin Kano shawara

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Kwamitin karɓar mulki na NNPP na 2023 a jihar Kano ya gargadi daukacin shugabannin kananan hukumomi 44 da manyan ma’aikatan su da su guji bari a yi amfani da kudaden kananan hukumomin su ta hanyar data sabawa doka.

 

” Mun Sami labarin ana shirin amfani da kudaden kananan hukumomi wajen kammala zabuka a Inda basu kammala ba, a wasu kananan hukumomin a jihar kano, wanda yin hakan ba dai-dai bane Kuma ya sabawa doka.

 

Ganduje ya kore mu daga APC, mu kuma mu ka yi masa ritaya daga siyasar Kano – Abdulmumini Kofa

Shugaban kwamitin Dr. Abdullahi Bafa Bichi ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24.

 

Yace baza su lamunci yin almubazzaranci da dukiyoyin al’ummar jihar kano ba, don haka suke baiwa shugabannin kananan hukumomin da su guji yin hakan , domin gwamnati mai jiran gado bazata bari a ɗauki kudaden al’umma a yiwa wata jam’iyyar siyasa aiki ba .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...