Tun bayan yaƙin basasa, Najeriya bata ta ba fuskantar rarrabuwar kawuna kamar yanzu ba – Sanusi

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

Khalifan Tijjaniyya, Muhammadu Sanusi II ya yi gargaɗi cewa Najeriya ta fi fama da rarrabuwar kai saboda ƙabilanci da bambancin addini tun bayan yaƙin Biafra fiye da shekara 50 da ta wuce.

Da yake jawabi a wani taro a Legas, Muhammadu Sanusi wanda ya ce “ba na tunanin Najeriya ta taɓa kasancewa a mawuyacin yanayi kamar yanzu tun bayan yaƙin basasa. Muna da ƙalubale game da aikin gina ƙasar nan.

Sarkin Kano ya Jagoranci Sallar Jana’izar Matar Gwamnan Kano na farko

Ya ce Najeriya tana fama da bambance-bambancen addini da na ƙabilanci.

Mun yi takaicin yadda muka rasa kujerar gwamnan kano – APC

“Muna da tattalin arzikin da ke fuskantar taɓarɓarewa kuma abin takaici, da alama muna fama da ƙarancin shugabanci na gari.”

Kalaman tsohon gwamnan CBN ɗin na zuwa ne yayin da Shugaba Muhammadu Buhari ke shirye-shiryen miƙa mulki ga Bola Tinubu.

Tinubu ne ya yi nasara a kan manyan abokan takararsa – Atiku Abubakar da Peter Obi a zaɓen shugaban ƙasar mai zafi da aka yi a watan Fabrairu.

Atiku da Obi sun yi fatali da sakamakon zaɓen, kuma tuni suka shigar da ƙara a kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...