Sarkin Gaya ya nada Sabon Dagacin Garin Gumakka

Date:

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 

Mai martaba sarkin gaya Alh Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya nada Malam Muhajid Bello Idris a matsayin sabon dagacin garin gumakka dake cikin karamar hukumar warawa.

 

Nadin nasa ya biyo bayan rasuwar mahaifinsa tsohon dagacin garin na gumakkan Mal bello Idris.

 

Sarkin Kano ya Jagoranci Sallar Jana’izar Matar Gwamnan Kano na farko

Mai martaba sarkin ya hori sabon dagacin da ya rike amanar al’umma da kuma sauraren koken su a koda yaushe .

 

Mun yi takaicin yadda muka rasa kujerar gwamnan kano – APC

“Muna horonka da ka guji shiga duk wata harka ta rashin gaskiya, sannan ka haɗa kai da sauran al’ummar ka wajen tabbatar da zaman lafiya da inganta Ilimin ‘ya’yan mu”. Inji Sarkin Gaya

 

Shi ma sabon dagacin garin gumakkan ya godewa Allah da ya nuna masa wannan Rana da Kuma Mai martaba sarkin na gaya

 

Ya kuma roki hadin kan al’ummar da zai jagoranta tare da rokon su da su taya shi da addu’o’in Allah ya kama masa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...