Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna ya taya Abba Gida-gida Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karɓi Kaddarar faɗuwa zaɓe tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano.

 

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.

 

INEC ta baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zaben gwamnan Kano

” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna

 

Yace dama ya fada a baya cewa zai karɓi Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaɓaɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...