Ba zan bari Matana, da ‘Yayana su shiga sha’anin mulki na ba – Abba Gida-Gida

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf (wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida) na jam’iyyar NNPP ya ce matansa da ‘ya’yansa ba za su shiga sabgar mulkin da zai yi jihar kano ba.

 

Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen karbar takardar shaidar lashe zabe a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta ke kano.

INEC ta baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zaben gwamnan Kano

Zababben gwamnan ya ce ba zai bari ‘yan uwansa su yi wani tasiri a harkokin mulkin sa a lokacin gwamnatin sa ba, saboda ba tare suka yi rantsuwar kama aiki da shi ba.

 

“Mata na ba za su shiga harkokin mulkina ba. ‘Ya’yana ba za su shiga cikin harkokin mulki ba. Kuma zan iya baku tabbacin cewa haka shima mataimakina.” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...