Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna ya taya Abba Gida-gida Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karɓi Kaddarar faɗuwa zaɓe tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano.

 

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.

 

INEC ta baiwa Abba Gida-gida Shaidar lashe zaben gwamnan Kano

” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna

 

Yace dama ya fada a baya cewa zai karɓi Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaɓaɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 

Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...