2023: Zan magance kishirwar rashin wakilci na gari ga al’ummar Kura Madobi da garun mallam a Majalisar wakilai – Musa Iliyasu Kwankwaso

Date:

Daga Nura Abubakar

 

Dan takarar wakilcin kura madobi da garin Mallam a jam’iyyar APC Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso ya sha alwashin da zarar yaje Majalisar wakilai ta kasa zai magance takaicin rashin wakilci na gari da al’ummar yankin suka dade suna fama da shi shekara da shekaru.

 

Musa Iliyasu Kwankwaso wanda yake shi ne Sarkin yaƙin Masarautar karaye yace ya tanadi kudirori wadanda zai Sanya a gaba da zarar yaje majalisa, Inda yace ya fahimci Rashin tanadin abun da za’a yiwa al’ummar yankin ne yasa suka tsinci kansu cikin halin da suke.

Kotu ta Fara Sauraron Shari’ar Muhd Abacha da Shugabannin PDP na mazabar sa

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da Kadaura24 a ofishinsa, abubuwan da zai sanya a gaba idan mutanen kura madobi da garun Mallam sun zabe shi a matsayin wakilinsu a majalisar wakilai ta kasa .

 

” Akwai kudirori da Zamu je da su majalisar wadanda idan suka tabbata zamu inganta Rayuwar al’ummar da zamu wakilta musamman ta fuskar Noma wanda dama da shi muka shahara a wannan yakin namu”. Inji Musa Iliyasu

 

 

Yace kudirin sa na farko idan yaje majalisa shi ne zai gabatar da kudirin yadda za’a Kara inganta harkokin noma a yankin da Kuma tsarin yadda manoma zasu rage yawan asarar da suke yi idan sun noma, wanda hakan na karyar da gwiwar manoma .

 

“Nasan idan Allah ya taimaka kudirin ya wuce to babu shakka, za’a sami Karuwar arziki da kawaitar shi a cikin al’umma, Kuma hakan zai Kara tabbatar da yankin mu a matsayin cibiyar noma ta kasa da arewa baki daya”. A cewar Kwankwaso

Muna Cikin mawuyacin halin sakamakon lalacewar hanyar garinmu – Mutanen Garin Jar kuka

Yace ba wai yana nufin noma shinkafa kawai ba, a’a yana nufin ingata duk wani nau’in abu da ake shukawa ya fito a yankin tsakanin rani da damina.

 

Akwai cigaban tattaunawar tana nan tafe a nan gaba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...

Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Daga Sharifiya Abubakar   Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro...

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

  Yusuf Galambi dan majalisar wakilai ya sauya sheka daga...