Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Date:

Daga Sharifiya Abubakar

 

Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro da bayanan sirri ta duniya (PI-SF) ta nada tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, matsayin Daraktan Hulɗa da ‘yan majalisar Afrika kuma memba a kwamitin zartarwa na kungiyar.

Nadin nasa na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na duniya dan majalisar Amurka Robert Pittenger ya sanyawa hannu ranar 4 ga Fabarairun 2025.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta kara da cewa, jajircewa da kuma kwarewarsa wajen bunkasar harkokin tsaro a fadin duniya ya sanya ya zama mafi chanchanta da mukamin.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

Darakta Sha’aban zai mayarda hankali wajen Inganta hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin majalisun Afrika don tunkarar matsalolin tsaro da gudanarwa, hadi da kawo ƙarin ‘yan majalisa, jami’an tsaro, da masu tsara manufofi daga Afrika cikin tarukan kungiyar.

Kazalika sabon daraktan zai samar da fagen tattaunawa tare da majalisun Afrika don inganta haɗin kai kan tsaro, leƙen asiri, tsaron yanar gizo, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...