Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Date:

Daga Sharifiya Abubakar

 

Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro da bayanan sirri ta duniya (PI-SF) ta nada tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, matsayin Daraktan Hulɗa da ‘yan majalisar Afrika kuma memba a kwamitin zartarwa na kungiyar.

Nadin nasa na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na duniya dan majalisar Amurka Robert Pittenger ya sanyawa hannu ranar 4 ga Fabarairun 2025.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta kara da cewa, jajircewa da kuma kwarewarsa wajen bunkasar harkokin tsaro a fadin duniya ya sanya ya zama mafi chanchanta da mukamin.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

Darakta Sha’aban zai mayarda hankali wajen Inganta hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin majalisun Afrika don tunkarar matsalolin tsaro da gudanarwa, hadi da kawo ƙarin ‘yan majalisa, jami’an tsaro, da masu tsara manufofi daga Afrika cikin tarukan kungiyar.

Kazalika sabon daraktan zai samar da fagen tattaunawa tare da majalisun Afrika don inganta haɗin kai kan tsaro, leƙen asiri, tsaron yanar gizo, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...