Ganduje ya tafi Kasar Amurka, ya mika mulki ga Gawuna

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
 Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya tafi kasar Amurka inda yake halartar wani shiri na tsawon mako Guda akan jagoranci.
  KADAURA24 ta rawaito Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa Gwamna Ganduje na halartar wani shiri na inganta jagoranci na kwarai a makarantar kasuwanci ta Harvard da ke Boston.
 Ya ce gwamnan ya mika mulki kuma ya ba mataimakin gwamna Dakta Nasir Yusuf Gawuna cikakkiyar damar zama mukaddashin gwamnan jihar.
 Sanarwar ta kara da cewa duk wata harkokin mulki daga yanzu sai an bi ta ofishin mataimakin gwamna domin daukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...