Yan Bindiga sun Kona Motar haya da Mutane 42 a Jihar Sokoto

Date:

Rahotanni daga jihar Sokoto na cewa ‘yan bindiga sun kona wata motar fasinja dauke da mutum 42.

Rahotannin sun ce fasinjojin sun fito ne daga karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar domin yin ƙaura zuwa wasu yankunan Najeriya, saboda ta’azzarar ayyukan ‘yan bindiga a inda suke.

Wasu shaidu sun cewa BBC lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 na safiyar ranar Litinin.

“Motar ɗauke da fasinjojin ta tashi daga Sabon Birni, ta yi tafiyar da bai fi kilomita shida ba zuwa kauyen Gidan Bawa inda wannan masifa ta afka mata,” kamar yadda wadanda suka yi aikin ceton suka bayyana wa BBC.

Tuni dai aka yi jana’ziar mamata in ji shaidu.

BBC ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rundunar ƴan sandan jihar, amma haƙarsu ba ta ci cimma ruwa ba, ko da suka kira kakakin, wayarsa a kashe take.

Kazalika mun kira kwamishinan tsaro na jihar har sau uku shi ma bai ɗauka ba.

Tuni dai aka yi jana’ziar mamata in ji shaidu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...