Fati Muhammad ta sake dawowa Kanywood, bayan Shekaru 14 da barin masana’antar

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

 

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa Fati Muhammad ta dawo Kannywood bayan shafe shekaru goma sha hudu da daina sana’ar.

Dawowar Fati ta kasance tare da fatan alheri daga masoyanta da masoyan fina-finan Hausa.

Ta dawo ne a matsayin mai shirya fina-finai kamar yadda wata ‘yar gajeriyar sanarwa ta bayyana a shafin Facebook na ‘Kannywoodcelebrities.

A Ranar talatar nan dai sabbin hotunan Jarumar sun karade shafukan Sada Zumunta musamman Facebook da instegram Wanda hakan ke nuni da Cewa al’umma Suna farin Ciki da dawowarta harkar Fina-finan Hausa.

KADAI ta rawaito an dai nuna hoton Fati Muhd a zaune kan Wata kujera yayin da ake daukar wani sabon fim Wanda zata taka rawa a Cikin sa, Kuma za a iya Cewa Shirin shi ne na Farko bayan dawowarta harkar Fina-finan Hausa.

Fati ‘yar asalin jihar Adamawa ta fara harkar fim tun tana karama, Fina-finan ta da suka yi fice a Cikin su sun hada da Sangaya, Zarge, Marainiya, Mujadala, Kudiri, Tutar So, Garwashi, Tawakkali, Gasa, Abadan Da’iman, Zo mu Zauna, Tangarda, Hujja, Al’ajabi, Halacci, Samodara, Zumunci, Murmushin Alkawari, Gimbiya, Bakandamiya, Taskar Rayuwa, Babban Gari da dai Sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...