Rashin Sarkin Ban Kano Babban Rashin ga Kasar nan – Alhassan Ado

Date:

Daga Khadija Abdullahi Adam

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar wakilai kuma Dan Majalisar Mai wakiltar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada Hon Alhassan Ado Doguwa ya aike da Sakon ta’aziyyar Sarkin Ban Kano Alhaji Mukhtar Adnan .
Cikin Wata Sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Majalisar wakilai Auwal Ali Sufi ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.
Sanarwa tace Sarkin Ban Kano uba ne a Jihar Kano da Nigeria baki Wanda ya bayar da gagarumar Gudunmawa wajen taimakawa al’umma ta fuskoki da dama.
Doguwa yace Yana Mika ta’aziyyar sa ga Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Bichi da al’ummar Ƙaramar Hukumar Danbatta da al’ummar Jihar Kano baki daya .
Ya Kuma Yi Masa fatan samun rahamar Ubangiji subhanahu wata’ala tare da fatan iyalansa al’ummar sa zasu jure rashinsa .

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...