Rashin Sarkin Ban Kano Babban Rashin ga Kasar nan – Alhassan Ado

Date:

Daga Khadija Abdullahi Adam

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar wakilai kuma Dan Majalisar Mai wakiltar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada Hon Alhassan Ado Doguwa ya aike da Sakon ta’aziyyar Sarkin Ban Kano Alhaji Mukhtar Adnan .
Cikin Wata Sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Majalisar wakilai Auwal Ali Sufi ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.
Sanarwa tace Sarkin Ban Kano uba ne a Jihar Kano da Nigeria baki Wanda ya bayar da gagarumar Gudunmawa wajen taimakawa al’umma ta fuskoki da dama.
Doguwa yace Yana Mika ta’aziyyar sa ga Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Bichi da al’ummar Ƙaramar Hukumar Danbatta da al’ummar Jihar Kano baki daya .
Ya Kuma Yi Masa fatan samun rahamar Ubangiji subhanahu wata’ala tare da fatan iyalansa al’ummar sa zasu jure rashinsa .

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...