Ka da ku karaya, za ku cimma burinkan ku – Buhari ya fadawa Matasa

Date:

Daga Nura Abubakar
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci matasan Najeriya da su ci gaba da jajircewa kada su gajiya wajen cimma manufofinsu.
 Ya kuma bukace su da kada su gaji wajen fuskantar kalubale, inda ya ba su tabbacin za su kai ga Samun nasara.
 Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne jawabi lokacin da yake bude taron matasa na kasa na kwanaki uku a babban filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja.
 Da yake Kara musu gwarin gwiwa la’akari da gagarumin damar, kirkire-kirkire da sana’o’in matasan Najeriya, Shugaba Buhari ya ce sana’o’in nishadi da kade-kade, wasanni, fasaha da sauran fannoni Sune Waɗanda matasa Suka fi Maida hankali akan su ,yace zasu taimaka sosai Wajen bunkasa tattalin arzikin su da Kuma basu damar cimma burikansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...