Ka da ku karaya, za ku cimma burinkan ku – Buhari ya fadawa Matasa

Date:

Daga Nura Abubakar
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci matasan Najeriya da su ci gaba da jajircewa kada su gajiya wajen cimma manufofinsu.
 Ya kuma bukace su da kada su gaji wajen fuskantar kalubale, inda ya ba su tabbacin za su kai ga Samun nasara.
 Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne jawabi lokacin da yake bude taron matasa na kasa na kwanaki uku a babban filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja.
 Da yake Kara musu gwarin gwiwa la’akari da gagarumin damar, kirkire-kirkire da sana’o’in matasan Najeriya, Shugaba Buhari ya ce sana’o’in nishadi da kade-kade, wasanni, fasaha da sauran fannoni Sune Waɗanda matasa Suka fi Maida hankali akan su ,yace zasu taimaka sosai Wajen bunkasa tattalin arzikin su da Kuma basu damar cimma burikansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...