Yanzu-Yanzu: An Kawo Karshen Corona a Kasar Saudia

Date:

Daga Nusiba Rabi’u Yusuf
Hukumomi a Kasar Mai tsarki sun bayyana cewa bayan Samun nasarar da ake a yaki da Annubar Covid-19, yanzu haka za’a sassauta Matakai Masu tsari da aka dauka a Masallatan Haramin Makka da Madina.
Ma’aikatar Cikin gida ta Kasar Saudia ita ce ta bada Sanarwar hakan Kamar yadda Kamfanin dillacin labarai na Routers ya rawaito.
Sanarwar tace gwamnatin za ta dage matakan bada tazara kuma za ta ba da damar Cika a  Masallatan Harami biyu na Makka da Madina ga wadanda suka karbi cikakkiyar allurar rigakafi Corona.
 Hukumomin sun ce an soke duk Wata dokar Corona data hana mutane haduwa a wuraren taro, motocin haya,gidajen abinci da sinima.
Haka Kuma sun ce Sanya takunkumin fuska bai zama tilas ba a wuraren taruwar jama’a Amma fa ga Waɗanda Suka yi Allurar rigakafin Corona Kashi na 1 da na 2.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...