Yanzu-Yanzu: An Kawo Karshen Corona a Kasar Saudia

Date:

Daga Nusiba Rabi’u Yusuf
Hukumomi a Kasar Mai tsarki sun bayyana cewa bayan Samun nasarar da ake a yaki da Annubar Covid-19, yanzu haka za’a sassauta Matakai Masu tsari da aka dauka a Masallatan Haramin Makka da Madina.
Ma’aikatar Cikin gida ta Kasar Saudia ita ce ta bada Sanarwar hakan Kamar yadda Kamfanin dillacin labarai na Routers ya rawaito.
Sanarwar tace gwamnatin za ta dage matakan bada tazara kuma za ta ba da damar Cika a  Masallatan Harami biyu na Makka da Madina ga wadanda suka karbi cikakkiyar allurar rigakafi Corona.
 Hukumomin sun ce an soke duk Wata dokar Corona data hana mutane haduwa a wuraren taro, motocin haya,gidajen abinci da sinima.
Haka Kuma sun ce Sanya takunkumin fuska bai zama tilas ba a wuraren taruwar jama’a Amma fa ga Waɗanda Suka yi Allurar rigakafin Corona Kashi na 1 da na 2.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...