Maulud : Buhari ya aiyna ranar Talata a Matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Talata 19 ga Oktoba, 2021 a matsayin Ranar Hutu don murnar bikin Maulidin na wannan shekarar don tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (Sallal-lahu alaihi wa sallam).
 Ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, wanda ya yi wannan sanarwar a madadin Gwamnatin Tarayya, yana ya taya dukkan musulmin da ke cikin gida Nigeria da na kasashen waje murnar bikin wannan shekarar.
 Ya shawarci dukkan ‘yan Najeriya da su sanya soyayya, hakuri da juriya a rayuwar su Kamar yadda wadanda su ne dabi’un Annabi Muhammadu (saw), Inda ya kara da cewa yin hakan zai tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar.
 Ogbeni Aregbesola ya umarci ‘yan Najeriya, musamman Musulmai, da su guji tashin hankali, rashin bin doka da sauran ayyukan da basu kamata ba.
 Minista yayi kira da a dakatar da duk wasu abubuwan da ke kawo rarrabuwar kawuna a fadin kasar, ya Kuma bukaci dukkan ‘yan Najeriya musamman matasa, da su rungumi dabi’un na gari Inda yace Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na kokarin gina kasa don cigaban al’ummar Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...