Maulud : Buhari ya aiyna ranar Talata a Matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Talata 19 ga Oktoba, 2021 a matsayin Ranar Hutu don murnar bikin Maulidin na wannan shekarar don tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (Sallal-lahu alaihi wa sallam).
 Ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, wanda ya yi wannan sanarwar a madadin Gwamnatin Tarayya, yana ya taya dukkan musulmin da ke cikin gida Nigeria da na kasashen waje murnar bikin wannan shekarar.
 Ya shawarci dukkan ‘yan Najeriya da su sanya soyayya, hakuri da juriya a rayuwar su Kamar yadda wadanda su ne dabi’un Annabi Muhammadu (saw), Inda ya kara da cewa yin hakan zai tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar.
 Ogbeni Aregbesola ya umarci ‘yan Najeriya, musamman Musulmai, da su guji tashin hankali, rashin bin doka da sauran ayyukan da basu kamata ba.
 Minista yayi kira da a dakatar da duk wasu abubuwan da ke kawo rarrabuwar kawuna a fadin kasar, ya Kuma bukaci dukkan ‘yan Najeriya musamman matasa, da su rungumi dabi’un na gari Inda yace Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na kokarin gina kasa don cigaban al’ummar Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...