Har Yanzu Malam Ibrahim Khalil Muka Sani a Shugabancin Majalisar Malamai – inji Manyan Malaman Kano

Date:

Daga Halima M Abubakar

 

Jagororin Gamayyar kungiyoyin Malamai da Kungiyoyin addinin Musulunci na jihar kano sun yi watsi da Sanarwar tsige Malam Ibrahim Khalil Daga Shugabancin Majalisar Malamai ta jihar Kano.

 

Kadaura24 ta rawaito hakan na kunshe ne Cikin Wata sanarwa da Sakataren Kungiyar Dr. Sa’eed Ahmad Dukawa ya Sanyawa hannu Kuma aka rabawa Manema labarai a Kano.
Sanarwar tace wancan Mataki da aka dauka na cire Sheikh Ibrahim Khalil anyi shi bada Sanin jagororin ba, Kuma haka babu abun da Zai haifar sai fitina a tsakanin Malamai dama jihar kano daki daya.
Sanarwar ta bukaci al’umma suyi watsi da waccen Sanarwa da aka fitar tun da fari, Sannan Sanarwar tace sun dauki Wannan Matakin ne bisa Amincewa jagororin Qadirriyya da Izala dama Tijjaniya Kamar su:
Farfesa Musa Borodo, Sheikh Khalifa Karibullah Nasiru Kabara, Sheikh Abdulwahab Abdullah, Sheikh Ibrahim Shehu Maihula, Farfesa Muhd Babangida , Dr. Bashir Aliyu Umar, Imam Muhd Nasir Adam da Kuma Dr Mu’azzali Ibrahim Maibushira.
Daga Karshe sun tabbatar da Cewa har Yanzu Sheikh Ibrahim Khalil shi Suka Sani a Matsayin Shugaban Majalisar Malaman jihar Kano domin hakan ne Zai tabbatar da Zaman lafiyar da ake dashi a Kano.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...