Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi ta jihar Kano da su fadada ayyukansu ta yadda za’a tallafawa al’umma wajen ba da Zakka yadda ya Kamata.

Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin ayarin shugabannin Hukumar Zakka da Hubusi ta jihar Kano a Fadar sa

Yana mai cewar bada Zakka na matsayin wata hanya ta sauke nauyi daga cikin rukunan Musulunci .

InShot 20250309 102403344
Talla

” Muna fatan za ku fadada aiyukan ta yadda mutane da yawa za su amfana da zakkar, dama manufar zakka ita ce kawarwa ko rage talauci a cikin al’umma”.

Sarki Sanusi II ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don baiwa hukumar zakkar dukkanin wasu shawarwari da hadin kai da goyon baya don inganta aiyukansu.

A Jawabin Sa tun da Farko, Shugaban Hukumar zakka da hubusin Barista Habibu Dan Almajir ya ce sun kai ziyara fadar Sarkin ne don neman goyon bayan Masarautar Kano bisa irin ayyukan hukumar.

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

” Mun zo wannan fadar ne don neman shawarwari da goyon bayan mai martaba ta yadda za mu inganta aiyukan wannan hukumar.

Wakilinmu ya bamu labarin cewar Shugaban Hukumar Barista Habibu Dan Almajir ya Kuma yabawa Masarautar Kano bisa irin Tarbar da akayi Musu.

Shugaban hukumar zakka da hubsin Barr. Habib Dan Almajiri ya ziyarci Sarkin tare da Commissioner l Malan Nafi’u! Umar Harazumi Da Commissioner II Malan Ali Mustapha Kuraysh da Members tare Da Daraktocin hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...