Rashin kyakykyawan albashi, Musgunawa sun sa wani Ma’aikacin Nas Radio Yola ya ajiye Aikinsa

Date:

Gidan radion NAS Fm Yola ta dauko hanyar rasa ma’akatanta saboda rage albashi da kuma rikon sakainar kashin da takeyiwa ma’aikatanta.

A takardar ajiye aikin da ya aikawa Hukumar gudanarwar gidan radio, daya daga cikin ma’aikacin gidan redion Zaiyad Ismail wanda shine yake gabatar da shirin #Ina_Matasa yace ya ajiye aiki ne saboda rashin adalcin da akeyi, kana yace a ranar Asabar da ta gabata ya gayyaci Dan Majalisan Jaha mai wakiltar Karamar Hukumar Gombi Hon. Japhet Kefas domin gabatar da shiri akan samun ‘yancin Najeria, suna cikin gabatar da shirin kwatsam shugaban kafar yace ya dakatar da shirin, a saka wani shiri daban.

Zaiyad yace ya kira shugaban kafar ta a waya akan dalilin da yasa akace ya dakatar da shirin alhali awa daya ne aka debawa shirin kuma minti talatin kawai yayi? Shugaban kafar yace ai an rage lokacin shirin ne, ba irin rokon da baiyi masa ba akan ya barshi ya karasa shirin tunda ya gayyaci babban bako, amma shugaban yaki.

Ya kara da cewa hukumar gudanarwa ta Nas Fm karkashin jagorancin Musa Waziri Hardawa yana nuna banbanci tsakanin ma’aikata, inda zakaga mai kwalin Difloma yafi mai Degree albashi.

Zaiyad Ismail yace akwai abubuwa da dama da ake aikatawa a wannan gidan radion wanda ya sabawa ka’ida, kuma wanda ya assasa gidan radion baida labarin duk abubuwan da yake faruwa.

Majiyarmu tayi kokarin Jin ta bakin Shugaban Gidan Radio Amma wayarsa taba shiga har Lokacin hada Wannan rahotannon.

13 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...