Nafdac ta rufe wasu Kamfanin Yogot 4 a kaduna

Date:

Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa, NAFDAC, a jihar Kaduna ta rufe wasu cibiyoyi hudu da suke aikin samar da madarar yogot ba tare da rajista ba.
 Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Nasiru Mato ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ranar Juma’a a Kaduna.
 Mato ya ce hukumar ta rufe wuraren ne yayin da take zagayen Sanya idonu a  jihar don bankado Masu Aiki ba bisa ka’ida ba Kamar yadda Wadancan suke yi. Yace sun same su Suna aiki da kayiyaki mass inganci, rashin tsaftar muhalli, da aiki da tsohon lasisin da wa’adin su ya kare.
 Ya ce aikin sa ido wani bangare ne na matakan da hukumar ta ke dauka a jihar don tabbatar da cewa kmafanoni Suna Amfani da Sinadarai Masu inganci da tsafta da dai Sauransu.
 “Dangane da abin da ya gabata, muna so mu yi amfani da wannan damar don jaddada cewa dole ne a kiyaye tare da bin ƙa’idojin aiki ga masu samar da yoghurt da sauran abubuwan sha na ruwa don kare lafiyar masu amfani da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...