2021 Ranar Malamai : Matsalar Rashin Karin girma ce Babbar Matsalar mu a Kano

Date:

Daga Halima M Abubakar

Shugaban Kungiyar Malaman makarantu ta Kasa reshen jihar Kano com. Muhd Hambali Kura ya bayyana cewa Babbar Matsalar da malaman makaranta suke fuskanta a jihar Kano bai wuce Rashin Karin girma ba.

Com. Muhd Hambali ya bayyana hakan ne Yayin da yake ganawa da Jaridar Kadaura24 a Wani bangare na bikin Ranar Malamai ta duniya ta Shekara ta 2021.

Com. Hambali yace a shekarun baya gwamnatin Kano ta rage Wannan matsala ,Amma Yanzu ta sake dawowa domin akwai Malamai Masu tarin yawa da suke bukatar Karin girman bayan kuma lokacin yi musu Karin yayi wasuma ya wuce.

Ya bukaci Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje Daya duba koken nasu ya Magance musu Matsalar,Inda yace Magance Matsalar zata taimakawa Malaman su Sami karkashin baiwa dalibai Ilimi Mai inganci.

Da yake taya Malaman Murnar zagayowar Wannan Rana Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya yabawa Malaman bisa Gudunmawar da suke bayarwa don cigaban ilima a Kano.

Gwamnan ya bayyana irin kokarin da Gwamnatin Kano keyi na inganta harkokin Ilimi,Sannan ya baiwa Malaman tabbacin za’a ciyar da wadanda suka chanchanta gaba nan bada dadewa ba.

Majalisar Dinkin duniya ce dai ta ware ranar 5 ga watan disamba na kowacce shekara ta zamo Ranar Malaman makarantu ta Duniya, domin yin duba kan Matsaloli da nasarorin da malaman makarantu suke fuskanta a Duniya don Magance Matsalolin.

12 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...