Rashin kyakykyawan albashi, Musgunawa sun sa wani Ma’aikacin Nas Radio Yola ya ajiye Aikinsa

Date:

Gidan radion NAS Fm Yola ta dauko hanyar rasa ma’akatanta saboda rage albashi da kuma rikon sakainar kashin da takeyiwa ma’aikatanta.

A takardar ajiye aikin da ya aikawa Hukumar gudanarwar gidan radio, daya daga cikin ma’aikacin gidan redion Zaiyad Ismail wanda shine yake gabatar da shirin #Ina_Matasa yace ya ajiye aiki ne saboda rashin adalcin da akeyi, kana yace a ranar Asabar da ta gabata ya gayyaci Dan Majalisan Jaha mai wakiltar Karamar Hukumar Gombi Hon. Japhet Kefas domin gabatar da shiri akan samun ‘yancin Najeria, suna cikin gabatar da shirin kwatsam shugaban kafar yace ya dakatar da shirin, a saka wani shiri daban.

Zaiyad yace ya kira shugaban kafar ta a waya akan dalilin da yasa akace ya dakatar da shirin alhali awa daya ne aka debawa shirin kuma minti talatin kawai yayi? Shugaban kafar yace ai an rage lokacin shirin ne, ba irin rokon da baiyi masa ba akan ya barshi ya karasa shirin tunda ya gayyaci babban bako, amma shugaban yaki.

Ya kara da cewa hukumar gudanarwa ta Nas Fm karkashin jagorancin Musa Waziri Hardawa yana nuna banbanci tsakanin ma’aikata, inda zakaga mai kwalin Difloma yafi mai Degree albashi.

Zaiyad Ismail yace akwai abubuwa da dama da ake aikatawa a wannan gidan radion wanda ya sabawa ka’ida, kuma wanda ya assasa gidan radion baida labarin duk abubuwan da yake faruwa.

Majiyarmu tayi kokarin Jin ta bakin Shugaban Gidan Radio Amma wayarsa taba shiga har Lokacin hada Wannan rahotannon.

13 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...