Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Date:

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da yajin aikin gargadi na makonni biyu da ta fara a makon da ya gabata a dukkan jami’o’in gwamnati a faɗin ƙasar.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Chris Piwuna, ne ya sanar da hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a babban ofishin ASUU da ke Abuja a ranar Laraba.

Farfesa Piwuna ya bayyana cewa an yanke wannan shawara ne bayan shiga tsakani daga Majalisar Dattawa tare da wasu masu ruwa da tsaki, domin samar da fahimtar juna tsakanin gwamnati da ƙungiyar.

Sai dai ya ƙara da cewa, Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta ASUU ta ba wa gwamnatin wa’adin wata guda domin magance matsalolin da suka haddasa yajin aikin, inda ya yi gargadin cewa ƙungiyar za ta ɗauki mataki mafi tsanani idan aka kasa cika alkawura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...