Mutane uku sun Jikkata sakamakon gobara a shagon siyar da Gas a Hotoro

Date:

Daga Sani Magaji Garko

Al’ummar Layin Garsan Fulani cikin Unguwar Hotoron Arewa a Karamar hukumar Nasarawa da ke nan Kano sun shiga cikin dimuwa sakamakon tashin Gora a shagon siyar da Gas.

Wani da abin ya faru a idon sa Malam Abdullahi ya bayyana wa manema labarai cewa wutar ta tashi ne sakamakon kan tukunyar gas ya da ki keken dinki.

Lamarin ya shigar da mautanen yankin cikin tsoro Wanda hakan ya sa makotan shagon guduwa daga gidajen su domin neman mafaka.

Wani shaidar gani da ido ya ce mutane uku sun sami raunuka ciki harda wata matar Aure dake makwabtaka da shagon, yayin da wutar ta tarwatsa masu kade-kaden bukukuwan aure a kusa da abin da ya faru.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin.

Saminu Yusif Abdullahi ya ce sun sami Kira daga wani Malam Anas Musa da misalin karfe 8:52 cewa wani shagon siyar da Gas ya kama da wuta a Hotoro tsamiyar Boka layin Garsan Fulani.

Kadaura24 ta rawaito cewa Saminu Yusuf ya ce suna samun lamarin suka yi gaggawar tura jami’an su inda cikin kankanin lokaci suka shawo kan matsalar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...