Ruwan Sama ya jefa makabartar Rimin kebe cikin mummunan hali

Date:


Daga Ibrahim Aminu Rimin kebe.

Makabartar unguwar Rimin kebe dake yankin karamar hukumar Ungogo tana Cikin Wani mummunan hali Sakamakon yadda ake Samun ruftawar kaburbura,

Wanda wannan alamarin ya faru ne a sakamakon ruwan da aka samu a daran Ranar Juma’ar data gabataj, lamarin ya sanya tarin kaburbura masu yawan gaske suka rufta.

Al’ummar yankin sun shaidawa Kadaura24 cewa sun rubuta takardar Neman daukin mahukun karamar hukumar ta Ungogo amma Kuma shiru kaji, Wanda a cewar shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Muhammad Sani hattama shugaban kwaminitin makabartar na jihar wato Malam Ado Kurawa yasan da wannan matsalar ta ruftawar kaburbura a makabartar a unguwar ta Riminkebe.

Lamarin dai a cewar Alhaji Sani ya zuwa yanzu babu abunda suke Bukata face kasar da zasu cike kaburburan da suke a bude a yanzu haka, ya Kara da cewar ya zuwa yanzu basu tantance adadin kaburburan da suke a bude ba.

Ya cewa a yanzu haka kasar data rage musu bata fi mangala uku ba, ba rantama har su shiga aikin rufe kaburburan.

Daga karshe shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Sani Muhammad yayi kira ga gwamnati a kowa ne mataki da kuma daidaikun al’umma Musamman mawadata dasu kaiwa makabartar dauki, ko Babu komai ita makarantar gidan kowa ce.

95 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...

Al’ummar Garin Riruwai da wani Kamfanin Hakar ma’adanai Sun Cimma Yarjejeniya Kan Ci gaban yankin

Kwamitin ci gaban Al’ummar garajn Riruwai da wani kamfanin...