Ruwan Sama ya jefa makabartar Rimin kebe cikin mummunan hali

Date:


Daga Ibrahim Aminu Rimin kebe.

Makabartar unguwar Rimin kebe dake yankin karamar hukumar Ungogo tana Cikin Wani mummunan hali Sakamakon yadda ake Samun ruftawar kaburbura,

Wanda wannan alamarin ya faru ne a sakamakon ruwan da aka samu a daran Ranar Juma’ar data gabataj, lamarin ya sanya tarin kaburbura masu yawan gaske suka rufta.

Al’ummar yankin sun shaidawa Kadaura24 cewa sun rubuta takardar Neman daukin mahukun karamar hukumar ta Ungogo amma Kuma shiru kaji, Wanda a cewar shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Muhammad Sani hattama shugaban kwaminitin makabartar na jihar wato Malam Ado Kurawa yasan da wannan matsalar ta ruftawar kaburbura a makabartar a unguwar ta Riminkebe.

Lamarin dai a cewar Alhaji Sani ya zuwa yanzu babu abunda suke Bukata face kasar da zasu cike kaburburan da suke a bude a yanzu haka, ya Kara da cewar ya zuwa yanzu basu tantance adadin kaburburan da suke a bude ba.

Ya cewa a yanzu haka kasar data rage musu bata fi mangala uku ba, ba rantama har su shiga aikin rufe kaburburan.

Daga karshe shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Sani Muhammad yayi kira ga gwamnati a kowa ne mataki da kuma daidaikun al’umma Musamman mawadata dasu kaiwa makabartar dauki, ko Babu komai ita makarantar gidan kowa ce.

95 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...