Ruwan Sama ya jefa makabartar Rimin kebe cikin mummunan hali

Date:


Daga Ibrahim Aminu Rimin kebe.

Makabartar unguwar Rimin kebe dake yankin karamar hukumar Ungogo tana Cikin Wani mummunan hali Sakamakon yadda ake Samun ruftawar kaburbura,

Wanda wannan alamarin ya faru ne a sakamakon ruwan da aka samu a daran Ranar Juma’ar data gabataj, lamarin ya sanya tarin kaburbura masu yawan gaske suka rufta.

Al’ummar yankin sun shaidawa Kadaura24 cewa sun rubuta takardar Neman daukin mahukun karamar hukumar ta Ungogo amma Kuma shiru kaji, Wanda a cewar shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Muhammad Sani hattama shugaban kwaminitin makabartar na jihar wato Malam Ado Kurawa yasan da wannan matsalar ta ruftawar kaburbura a makabartar a unguwar ta Riminkebe.

Lamarin dai a cewar Alhaji Sani ya zuwa yanzu babu abunda suke Bukata face kasar da zasu cike kaburburan da suke a bude a yanzu haka, ya Kara da cewar ya zuwa yanzu basu tantance adadin kaburburan da suke a bude ba.

Ya cewa a yanzu haka kasar data rage musu bata fi mangala uku ba, ba rantama har su shiga aikin rufe kaburburan.

Daga karshe shugaban kwaminitin makabartar unguwar Riminkebe Alhaji Sani Muhammad yayi kira ga gwamnati a kowa ne mataki da kuma daidaikun al’umma Musamman mawadata dasu kaiwa makabartar dauki, ko Babu komai ita makarantar gidan kowa ce.

95 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...