Babu Mai laifin da zamu bari – Buhari

Date:

Daga Surayya Abdullah Tukuntawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nuna bacin ransa kan kisan kiyashin da ake yi wa ‘yan kasar nan, ciki har da shugaban ‘yan sintiri da kuma shugaban Dabna, a kauyen Dugwaba da ke karamar hukumar Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban yana mayar da martani ne kan abin da ya faru a ranar Laraba, yana cewa, “Yadda ake nuna rashin imani da rashin tausayi ba za mu bari duk mai hannu ya tafi haka ba, duk wani mai laifi sai mun hukunta shi”.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga shugaban, Garba Shehu ya fitar shugaban ya bai wa jami’an tsaro umarnin “Su ninka kokarinsu da kuma matakan da suke dauka kan wadannan bata gari cikin gaggawa”.

Buhari ya kuma umarci ma’aikatar ba da agaji da ta duba abin da aka yi asara a yankin a kuma aika musu da taimakon gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...