Sallah: Shugaba Buhari ya bukaci a takaita bukukun Sallah Saboda Corona

Date:

Daga Aisha Uwais

 Yayin da Musulmai a Najeriya suka bi sahun sauran Musulmi a duniya wajen  shirye-shiryen bikin Karamar sallah  Shugaba Muhd Buhari ya bada umarnin  takaita dukkan bukukun saboda Annobar Coronavirus data addabi duniya.


 A cewar wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Mallam Garba Shehu Shugaban Kasar da Iyalansa da hadimansa, mambobin majalisar zartarwa da shugabannin hafsoshin tsaro wadanda suka zabi zama a Abuja za su hallarci sallah idi da karfe 09:00 na safe a fadar Shugaban kasa cikin bin ka’idojin kare Kai daga cutar COVID-19.


 Bayan haka Kuma Shugaban Kasar ba Zai karbi Masu zuwa Yi Masa Barka da sallah ba kamar yadda aka saba ,Inda ya umarci limamai Yan siyasa da Shugabanin gargajiya dasu gudanar da bukukun sallar a gidajen su don gudun yaduwar Annobar Coronavirus.


 Sanarwar ta nuna cewa Shugaba Buhari yana mika godiya ta musamman ga Ulama (Malaman Addinin Musulunci) da duk sauran shugabannin addini (Musulmi) wadanda ke ci gaba da yi wa kasar nan addu’o’in samun Zaman lafiya Mai dorewa.


 Shugaban, baya ga wannan, yana amfani da wannan dama don jajantawa duk wadanda suka rasa Yan uwansu Sakamakon Matsalolin tsaro dake faruwa a sassan kasar.


 Shugaban yana kira ga dukkan shugabanni da su ja kunnen matasan su tare da gargadin su kan amfani da su wajen tayar da fitina.

80 COMMENTS

  1. Усик Джошуа бій 25 вересня в Лондоні – все про поєдинок Энтони Джошуа Александр Усик Бой Усик – Джошуа пройдет 25 сентября в Лондоне. На кону в этом поединке будут стоять титулы чемпиона мира в супертяжелом весе по версиям ibf, wbo, wba и ibo, которыми владеет Джошуа.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rashin wadataccen Abinchi ne ke haifar matsalolin tsaro da tattalin arzikin a Nigeria – Shugaban ACreasal

Daga Kamal Umar   Babban jami’in Shirin bankin duniya mai kula...

Kungiyar kafafen yada labaran yanar gizo ta bukaci gwamnatin Kano ta gyara hanyoyin dake karkara

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kungiyar kafafen yada labarai na yanar...

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...